Majalisar Wakilai ta Bukaci Dakatar da Shugaban NMDPRA Saboda Zargin Rashin Gaskiya

top-news

Majalisar Wakilai ta Najeriya ta nemi a dakatar da Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta Najeriya (NMDPRA) domin gudanar da cikakken bincike kan zargin rashin gaskiya da ake yi wa Hukumar.

Honorabul Esosa Iyawe ne ya gabatar da wannan bukata a zauren majalisar, inda ya nuna damuwar sa game da matsalolin da kalaman batanci daga Shugaban Hukumar ya haifar.

Iyawe ya ce, "Dangote ya bukaci a yi gwajin kayayyakin su, inda aka gano cewa man dizal na Dangote yana dauke da sinadarin Sulfur mai matsakaicin 87.6 ppm (bangaren kowace miliyan), alhalin sauran samfuran diesel guda biyu da aka shigo da su suna dauke da Sulfur mai yawa sosai, har 1800 ppm da 2000 ppm. Wannan ya nuna rashin gaskiya a zargin da Shugaban NMDPRA ya yi.

"Hukumar NMDPRA na ba da lasisi ga wasu 'yan kasuwa da ke shigo da dizal mai tarin sulfur cikin Najeriya, wanda ke haifar da babbar illa ga lafiya da kuma asarar kudi mai yawa ga 'yan kasa."

Maganganun rashin tsaro na Shugaban NMDPRA, wanda aka karyata, ya haifar da fushin 'yan Najeriya, musamman ma wadanda suka ga hakan a matsayin zagon kasa ga matatun mai na cikin gida da kuma dagewar shigo da man fetur daga kasashen waje."

NNPC Advert